IQNA

Jagororin Musulmin Amurka Sun Yi Wa Trump Wasika

22:47 - December 06, 2016
Lambar Labari: 3481008
Bangaren kasa da kasa, jagororin kungiyoyin musulmin Amurka kusan 300 ne suka sa hannu kan wata wasi zuwa ga Trump dangane da rashin amincewa da siyasar kymar musulmi.
Kamfanin dillancin labaran kur'ani na iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na «Detroit News» cewa, shugabannin musumi kimanin 291 ne suka sanya hannu kan wasikar, wadda take nuna rashin amincewarsu da yadda ake neman a mayar da kymar musulmi wani halastaccen lamari a cikin kasar Amurka.

Jagororin msuulmin sun sanya hannu ne kan budaddiyar wasikar zuwa ga sabon shugaban kasar ta Amurka Donald Trump, suna masu jawo hankalinsa da ya dauki matakan da suka dace a lokacin shugabancinsa wajen ada kan dukkanin al'ummar Amurka duk kuwa da banbancin akidu da addinansu.

Kamar yadda kuma suka nuna rashin jin dadinsu kan yadda kyamar msuulmi ta karu matuka a kasar tun bayan da aka sanar da cewa ya lashe zaben shugaban kasar, sakamakon irin kalaman da ya rika furtawa alokacin yakin neman zaben na cin zarafi a kan musulmi, wanda ya bar mummann tasiri.

Kamar yadda kuma wasikar ta kirayi dukkanin al'ummar Amurka da su zama masu kiyaye kaidoji da dokokin kasa, domin kuwa dokar kasar ba yarje wa wani ya ci zarafin wani ba saboda akidarsa ko addininsa ba.

3551444


captcha