IQNA

Kwamitin Kare Hakkokin Musulmi A Ingila Ya Bukaci Da A Saki Sheikh Zakzaky

22:51 - July 01, 2021
Lambar Labari: 3486066
Tehran (IQNA) kwamitin kare hakkokin musulmi a kasar Ingila ya bukaci da a saki Sheikh Ibrahim Zakzaky a Najeriya.

A cikin wani bayani da ya fitar, kwamitin kare hakkokin musulmi a kasar Ingila ya bukaci da a saki Sheikh Ibrahim Zakzaky jagoran Harka Islamiyya a Najeriya, tare da mai dakinsa malama Zinat Ibrahim.

Wannan kira yana zuwa ne a lokacin da kotu ke sauraren shari'ar sheikh Zakzaky tare da mai dakinsa malama Zinat Ibrahim a Kaduna.

Babbar kotun jihar Kaduna a Najeriya, ta sanya ranar da 28 ga Yuli a matsayin ranar  yanke hukunci kan shari’ar da ake wa Sheikh Ibrahim Zakzaky da maidakinsa.

A zaman na ranar Alhamis, dukkan lauyoyin masu gabatar da kara da wadanda ake kara sun yi wa kotu bayani.

Babban lauya ga Malam El-Zakzaky, Femi Falana SAN, wanda ya yi magana da manema labarai jim kadan bayan dage zaman, ya bukaci Kotun da ta yanke hukunci a kan shari'ar wadanda yake karewa.

Tun a shekara ta 2015 ne dai ake tsare da malamin, da maidakinsa bayan farmakin da sojoji suka kaddamar a Zariya.

captcha