A cikin wani rahoto da gamayar kungiyoyin farar hula ta The coalition of Civil Society Organisations, da ke da mazauni a kasar Switzerland, da kuma wata kungiya ta kare hakkokin musulmi a Najeriya mai suna CEDRA suka fitar, sun bayyana cewa dole ne mahukunta su kare hakkokin mabiya mazhabar shi’a a Najeriya, suna yin ishara da magoya bayan Harka Islamiyya a kasar.
Bayanin na hadin gwiwar kungiyoyin ya bayyana hakkokin bil adama da kare ‘yancinsu na yin addinin da suka dama a matsayinsu na ‘yan kasa a matsayin halastaccen lamari a dokokin Najeriya, wanda suka yi ishara da ayar doka ta 33 a fasali na hudu a cikin kundin tsarin mulkin 1999.
A daya bangaren bayanin an yi ishara da farmakin da sojoji suka kaddamar a kan gidan jagoran Harka Islamiyya a Najeriya sheikh Ibrahim Zakzaky a karshen shekara ta 2015 a Zaria, wanda hakan ya yi sanadiyyar kisan daruruwan magoya bayansa a wurin, tare da kama shi tare da mai dakinsa da kuma daruruwan magoya bayansa, tare da yin tir da hakan, da kuma kiran mahukunta da su kawo karshen tsare shi.
3921870